An daidaita tsakanin malaman Jami'o'i da gwamnatin tarayya - Naija Crab Tech Blog

Search Blog

Artikel Terbaru

Featured

Saturday 9 September 2017

An daidaita tsakanin malaman Jami'o'i da gwamnatin tarayya


Kungiyar Malaman Jam'i'o'i ta Kasa, ta amince da yarjejeniyar da ta cimma a zamanta da gwamnatin tarayya, inda ta yarda za ta janye yajin aiki da zarar uwar kungiyar ta amince gaba dayan su.

A cimma wannan yarjejeniya ce bayan malaman sun shafe sa'o'i 12 da rabi su na tattaunawa an Abuja.

Har ila yau, a yayin wannan dogon zama da otherwise known as yi, a kuma kafa kwamiti mai kunshe da mutane bakwai a bangaren gwamnati da na bakwai a bangaren malaman Jami'o'in da zu duba yadda gwamnati za ta yi aiki da yarjejeniyar 2009, wacce dama rashin aiki da ita ne ya haifar da yajin aikin.

Kamar yadda Ministan Kwagago, Chris Ngige ya bayyana, ya ce kwamitin zai kunshi wakilai uku daga Ma'aikatar Ilmi, wasu uku daga Kungiyar Malaman Jami'o'i ta Kasa, sai kuma wakili daya daga bangaren Gwamnartin Tarayya, wanda shi ne zai kasance shugaban kwamiti.

Shugabannin kungiyar sun bayyana cewa duk da dai sun amince da yarjejeniyar, za su mika tayin da gwamnati ta yi musu, wurin mambobin su, daga nan bayan sati daya kuma su waiwayi gwamnatin tarayya dangane da matsayar su.

Shugaban kungiyar na kasa, Biodun Ogunyemi, ya shaida wa manema labarai cewa za su koma su tuntubi uwar kungiyar su gaba daya, daga nan kuma bayan mako guda su tunkari gwamnati da abin da su ka zartas.

A nasa bangaren, Ministan Ilmi, Adamu, ya ce a yarda za a biya wa kungiyar bukatun ta, kuma za su janye yajin aiki nan da mako guda bayan sun tuntubi sauran daukacin mambobinsu na fadin kasar nan.

A dai fara tattaunawar damisalin 1:38 na ranar Alhamis, otherwise known as kammala karfe 2:15 na daren Juma'a.

Want to Contact Us For Ads or Promotion? Click Here

Put your ad code here